Connect with us

News

INEC Dakatar Da Aikin Sake Tantance Rajistar Masu Zaɓe Har Zuwa Bayan Babban Zaɓen 2027

Published

on

Hukumar INEC mai shirya zaɓe a Najeriya ta sanar da dakatar da aikin sake tantance rajistar masu zaɓe har zuwa bayan zaɓen 2027 da ke tafe a shekara mai zuwa.

Wannan mataki ya biyo bayan tattaunawa da aka yiyi tsakanin masu ruwa da tsaki da kuma ƙusoshin hukumar.

SOKOTO: Hare-haren Ƴan Ta’adda Sun Tilasta Mazauna Ƙauyuka 21 Tserewa Daga Gidajensu

Tantance rajistar masu zaɓe na zama ɗaya daga cikin muhimman ayyukan hukumar, na tabbatar da sahihin zaɓe da kuma baiwa marasa rajistar zaɓe yin tasu rajistar don samun damar kaɗa ƙuri’a.

A yayin wannan aiki, akan tabbatar da suna da sauran bayanan mamallakin katin zaɓe da kuma yin duk wasu gyare-gyare idan an sami kuskure.

A cikin sanarwar da INEC ta fitar ta kuma jadaddawa ƴan ƙasar cewa tana kan bakanta na tabbatar da sahihi kuma ingantaccen zaɓe da zai zama abin kwatance a Najeriya dama idanun duniya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending