News
Babbar Sallah: Farashin Kayan Miya Ya Tashi Matuka A Kano
Yayin da al’ummar Musulmi a Jihar Kano ke ci gaba da shirye-shiryen gudanar da bikin Babbar Sallah, tashin gwauron zabo da farashin tumatir, barkono da sauran kayan miya ya haddasa damuwa tsakanin iyalai da masu sana’o’i a sassan jihar.
Binciken da aka gudanar a wasu manyan kasuwannin Kano, ciki har da Yankaba, Sabon Gari da Rimi, ya nuna yadda farashin kayan lambu da kayan miya ke ci gaba da tashi a daidai lokacin da jama’a ke shirin gudanar da bukukuwan Sallah.
Babbar Sallah: Farashin Kayan Miya Ya Tashi Matuka A Kano
A kasuwar Yankaba da ke kan titin Hadejia, an hangi dimbin masu saye suna yawo daga wannan shago zuwa wani domin neman saukin farashi, amma da yawa daga cikinsu sun bayyana rashin jin dadinsu kan yadda kayan suka yi tsada cikin kankanin lokaci.
Wata mai saye, Aisha Ibrahim, ta bayyana cewa farashin kayan ya zarce yadda ta zata.
“Farashin ya yi tsada sosai. Ina fatan idan na dawo gobe zan samu sauki, idan kuma bai sauka ba dole mu nemo wata hanya,” in ji ta.
Masu sana’ar sayar da kayan lambu sun danganta tashin farashin da karuwar bukatar kayan abinci yayin da ake tunkarar Babbar Sallah.
Wani dan kasuwa, Abdullahi Kwaki, ya ce buhun tattasai da ataruhu da ake sayarwa kan kusan N25,000 a watan da ya gabata yanzu ya kai tsakanin N110,000 zuwa N130,000.
Ya bayyana cewa duk da tsadar kayan, jama’a na ci gaba da saye saboda bukatar bukin Sallah.
Sai dai ya ce an samu sauki a farashin albasa, inda ta sauko daga kusan N70,000 zuwa kimanin N15,000.
Shi ma wani dan kasuwa, Aminu Sale, ya tabbatar da tashin farashin tumatir, yana mai cewa kwandon tumatir da ake sayarwa tsakanin N40,000 a baya yanzu ya kai kusan N110,000.
Duk da haka, wasu masu saye sun ce suna kokarin jurewa halin da ake ciki.
“Alhamdulillah, farashin ya tashi amma ba kamar yadda muka zata ba. Za mu yi hakuri da abin da Allah Ya hore mana,” in ji Safiya Yusuf.
A kasuwar Sabon Gari kuwa, ‘yan kasuwa sun ce farashin tumatir da barkono na ci gaba da tashin gwauron zabo sakamakon tsadar sufuri da karancin kayan da ke fitowa daga yankunan noma.
Malam Nasiru Bello, daya daga cikin ‘yan kasuwar, ya ce matsalar rashin tsaro da lalacewar hanyoyi na daga cikin abubuwan da suka haddasa tsadar kayan abinci.
“A baya muna sayar da kwandon tumatir kan N20,000, amma yanzu ya haura N38,000. Masu mota sun kara kudin dauko kaya, sannan kayan ba sa shigowa yadda aka saba,” in ji shi.
Mazauna jihar da suka zanta da manema labarai sun bayyana halin da ake ciki a matsayin abin damuwa, musamman ganin yadda jama’a ke fama da tsadar rayuwa da karin kudin sufuri.
Wani mazaunin Brigade Quarters, Suleiman Ado, ya ce iyalai da dama na iya kasa hada abinci mai armashi a lokacin bikin saboda tsadar kayan miya.
“Sallah ta zo amma rayuwa na kara tsananta. Ko kayan hada miya sun gagari talaka,” in ji shi.
A kasuwar Rimi kuwa, bincike ya nuna cewa kwandon tumatir da ake sayarwa tsakanin N18,000 zuwa N22,000 a baya yanzu ya kai kusan N40,000 gwargwadon inganci da girma.
Haka kuma karamin kwandon barkono ya tashi daga N10,000 zuwa kusan N18,000.
Masu sana’a sun danganta karin farashin da tsadar sufuri, sauyin yanayi da matsalolin tsaro da ke hana kayan gona isa kasuwanni yadda ya kamata.
Wata ‘yar kasuwa, Mariya Abdullahi, ta ce matsalar ta shafi masu saye da masu sayarwa baki daya.
“Mutane na zuwa kasuwa da fatan farashi zai sauka amma kullum sai ya kara tashi. Kudin kawo kaya daga gona sun yi yawa, wasu kayan ma suna lalacewa kafin su iso,” in ji ta.
Shi ma Ibrahim Sani ya ce rashin tsaro a wasu hanyoyin Arewa ya rage yawan kayan da ke shiga kasuwanni.
A cewarsa, tsoron hare-hare da tsadar noma sun sa manoma da dama rage yawan noman da suke yi.
Wata mazauniyar Yakasai, Fatima Usman, ta ce tsadar kayan abinci na kara jefa iyalai cikin matsin rayuwa.
“Tuni muna fama da tsadar shinkafa, mai da sauran kayan abinci. Yanzu kuma tumatir da barkono sun zama tamkar kayan alatu. Sallah ya kamata ta zama lokacin farin ciki, amma iyalai da dama na cikin damuwa,” in ji ta.
