Connect with us

News

RAYUKA NA CIKIN HAƊARI: Mazauna Bulbula-Gayawa Sun Koka Kan Jinkirin Aikin Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Published

on

IMG 20260712 WA0004

‎Mazauna unguwannin Bulbula da Gayawa da ke ƙananan hukumomin Ungogo da Nasarawa a Jihar Kano sun nuna damuwa kan jinkirin kammala aikin magance zaizayar ƙasa da ambaliya da ake gudanarwa a yankin, suna mai cewa jinkirin ya jefa rayuka da dukiyoyi cikin haɗari tare da ƙara tabarbarewar muhalli da matsalolin tsaro a yankin.

‎Mazauna yankin sun shaida cewa an ƙaddamar da aikin ne domin kawo ƙarshen matsalolin zaizayar ƙasa, ambaliya da lalacewar magudanan ruwa da suka addabi yankin tsawon shekaru.

KANO: Mata Masu Juna Biyu Na Fuskantar Barazana Sakamakon Lalacewar Cibiyar Lafiya A Dambatta

‎ Sai dai sun ce duk da muhimmancin aikin, har yanzu ba a kammala shi ba, lamarin da ke ci gaba da haddasa wahala ga al’umma.

‎Ɗaya daga cikin mazauna yankin, Ibrahim Sani, ya bayyana cewa jinkirin aikin ya jawo masa babban rashi, inda ya ce ya rasa ɗansa sakamakon haɗarin da ya alaƙanta da aikin da ba a kammala ba da kuma haƙar yashi ba bisa ƙa’ida ba a wurin aikin.

‎Haka kuma, wani mazaunin yankin ya ce wani ƙaramin yaro mai suna Muhammad Yusuf ya rasa ransa bayan ya faɗa cikin wani rami da aka haƙa a yankin aikin. A cewarsu, wuraren da ba a kammala aikin ba sun zama wuraren wasa ga yara, abin da ke jefa su cikin haɗari.

Advertisement

‎Mazauna yankin sun yi zargin cewa akalla yara biyu sun rasa rayukansu sakamakon irin waɗannan haɗura, yayin da wasu da dama suka samu raunuka ko kuma suka fuskanci matsalolin lafiya.

‎Sun kuma zargi wasu mutane daga wajen yankin da ci gaba da haƙar yashi ba bisa ƙa’ida ba a wurin aikin ta amfani da jakuna wajen jigilar yashin. Sun ce duk lokacin da aka hana su aiki da rana, sai su koma gudanar da aikin da dare.

‎Wasu daga cikin shugabannin al’umma sun ce gwamnatin jihar ta taɓa tallafa wa masu aikin jigilar yashi domin su koma wuraren da aka amince da su, amma wasu daga cikinsu sun yi watsi da wannan mataki tare da ci gaba da lalata wurin aikin.

‎Bugu da ƙari, mazauna yankin sun nuna damuwa kan matsalar tsaro, inda suka ce ramukan da aka bari sun zama mafakar masu aikata laifuka, ciki har da masu safarar miyagun ƙwayoyi da sauran bata-gari, lamarin da ke sa mutane tsoron zirga-zirga musamman da dare.

‎Da yake mayar da martani, Mai Kula da Ayyukan Shirin ACReSAL a Jihar Kano, Aminu Gidado Yusha’u, ya amince cewa an samu raguwar saurin aikin, amma ya ce hakan ya faru ne domin tabbatar da ingancin aikin.

‎Ya bayyana cewa gudanar da wasu muhimman ayyukan gini da suka haɗa da amfani da siminti, yashi da duwatsu a lokacin damina na iya raunana ginin tare da rage ɗorewarsa, saboda haka ana bin ƙa’idojin aikin injiniya domin tabbatar da inganci.

Advertisement

‎Aminu Gidado ya kuma ce zubar da shara ba tare da tsari ba cikin magudanan ruwa na daga cikin manyan ƙalubalen da ke jinkirta aikin. Ya ce duk lokacin da aka yi ruwan sama, ambaliya na kwaso shara da laka zuwa wurin aikin, abin da ke sa masu aikin share wurin kafin su ci gaba da aiki.‎

‎A cewarsa, lokacin da aka tsara aikin mai tsawon kusan kilomita uku, magudanan ruwa biyu ne kawai ke shiga babban magudanar. Sai dai sakamakon ci gaba da zaizayar ƙasa, yanzu adadin ya ƙaru zuwa 14, abin da ya sa aikin ya zama mafi wahala fiye da yadda aka tsara tun farko.

‎Ya kuma bayyana cewa binciken injiniyoyi ya nuna gadar da aka fi sani da Gada Mai-Doyi ta fara lalacewa kuma tana fuskantar barazanar ruftewa idan ba a ɗauki matakin gaggawa ba.

‎Saboda haka, ya ce Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ba da umarnin sake gina gadar a matsayin wani ɓangare na aikin domin kare rayuka da tabbatar da dorewar aikin magance ambaliya da zaizayar ƙasa.

‎A ƙarshe, Aminu Gidado ya roƙi mazauna yankin da su ƙara haƙuri, yana mai tabbatar da cewa ACReSAL, Ma’aikatar Muhalli ta Jihar Kano, kamfanin da ke gudanar da aikin da sauran abokan hulɗa suna aiki tukuru domin kammala aikin bisa ƙa’idodin aikin injiniya na ƙasa da ƙasa.

‎Ya kuma buƙaci al’umma su guji haƙar yashi ba bisa ƙa’ida ba da kuma zubar da shara cikin magudanan ruwa, yana mai bayyana cewa idan aka kammala aikin zai samar da mafita mai ɗorewa ga matsalolin ambaliya da zaizayar ƙasa a yankunan Bulbula da Gayawa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending