Connect with us

News

‎ICPC Ta Gano Wani Jami’in Da Ya Sanya Matarsa, ’Ya’yansa Da ’Yan Uwansa 14 Cikin Masu Karɓar Albashin Gwamnati

Published

on

ICPC chair Musa Aliyu e1731587252792

Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa da Sauran Laifukan da Suka Shafi Hakan (ICPC) ta ce ta gano wani jami’in gwamnati da ya sanya sunayen ’yan uwansa 14 cikin jerin masu karɓar albashin gwamnati.

‎Shugaban hukumar, Musa Aliyu, ya bayyana hakan ne a wajen taron Economic Confidential Lecture and National Spokespersons Award 2026, wanda aka gudanar a Abuja ranar Alhamis.

Janar Lucky Irabor Mai ritaya ya bukaci A Kama Sheikh Jingir Da Sheikh Gumi Kan Kalaman Tunzura Jama’a

‎Aliyu ya ce binciken da hukumar ta gudanar ya gano yadda wasu jami’an gwamnati ke amfani da guraben da ke cikin tsarin biyan albashi wajen shigar da sunayen ƙagaggun ma’aikata domin karɓar albashin da bai dace da su ba.

‎Ya ce a wani lamari da hukumar ta gano, mutum guda ya sanya sunayen mutane 14 daga cikin iyalinsa cikin jerin masu karɓar albashin gwamnati.

‎“Mun gano wani mutum da ya sanya mutane 14 daga cikin iyalinsa. Yana zaune a wani otel, yana karɓar albashi,” in ji shugaban ICPC.

Advertisement

‎Ya kuma bayyana cewa an gano wani mutum da ya sanya matarsa, ’yarsa, ɗansa da wasu ’yan uwansa cikin tsarin albashin gwamnati, inda shi kaɗai ke karɓar albashin mutane 13 a kowane wata.

 

THE CABLE 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending