Connect with us

News

Matasan Gawuna Sun Sauya Sheka, Sun Goyi Bayan Gwamna Abba

Published

on

1787681394451

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana aniyarta ta yin aiki tare da dukkanin mutane da ƙungiyoyin da ke da burin tabbatar da zaman lafiya da ci gaba mai ɗorewa a jihar.

Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida na jihar, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karɓi wasu tsoffin mambobin ƙungiyar matasa masu goyon bayan tsohon Mataimakin Gwamnan Kano, Dakta Nasiru Yusuf Gawuna.

Ba Na Siyasa Bisa Son Kai, Abin da Gwamna Abba Ya Ce Nake Yi —Waiya

Matasan sun sanar da ficewarsu daga tsohuwar ƙungiyar siyasar tasu, tare da bayyana goyon bayansu ga gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf.

Waiya ya ce gwamnatin jihar ta amince wa ƙungiyar ta yi aiki da sunan “Matasan Abba Gida-Gida”, tare da tabbatar da cewa za a ɗauke su cikin masu mara wa gwamnan baya da kuma wayar da kan jama’a kan manufofinsa na ci gaban jihar.

Ya ce gwamnati a shirye take ta yi aiki tare da ƙungiyar wajen aiwatar da shirye-shiryen da za su taimaka wajen ci gaban Kano.

Advertisement

Kwamishinan ya kuma bayyana cewa za a ba mambobin ƙungiyar damar shiga cikin shirin Tudun Muntshira (Safe Corridor) da sauran shirye-shiryen gwamnati da suka dace.

Ya buƙaci matasan da su yi amfani da ƙarfinsu da damar da suke da ita wajen tallafa wa zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban tattalin arzikin jihar.

Da yake jawabi, shugaban tsohuwar ƙungiyar matasan Gawuna, Malam Mustapha Abdullahi Dogo Chali, ya ce sun je wurin kwamishinan ne domin sanar da shi a hukumance cewa sun yanke shawarar goyon bayan Gwamna Abba Kabir Yusuf da gwamnatinsa.

Dogo Chali ya ce za su mayar da hankali wajen tallafa wa manufofin da za su ƙara wa gwamnan damar samun nasara a zaɓen gwamnan jihar na 2027.

Ya ce duk da cewa suna da burin ganin gwamnan ya samu nasara a zaɓen, za su kuma bayar da gudunmawa wajen ayyukan ci gaban jihar.

Ya roƙi gwamnatin Kano da ta ba ƙungiyar damar shiga cikin shirye-shiryen gwamnati, yana mai cewa mambobinsu a shirye suke su bayar da lokacinsu, ƙarfinsu da ƙwarewarsu wajen taimaka wa ci gaban jihar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending