News
Gwamnatin Ghana Ta Yi Watsi Da Tallafin Cedi Miliyan 20 Daga Kamfanin MTN
Gwamnatin Ghana ta yi watsi da tayin tallafin kuɗi har cedi miliyan 20 daga kamfanin sadarwa na MTN Ghana, wanda kamfanin ya yi niyyar bayarwa domin tallafa wa ’yan Ghana da hare-haren ƙyamar baƙi suka shafa a Afirka ta Kudu.
Ma’aikatar Harkokin Wajen Ghana ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Laraba, 26 ga Agusta, 2026, inda ta ce ta lura da rahotannin kafafen yaɗa labarai kan shirin MTN na bayar da tallafin.
Gwamnatin Ghana Ta Yi Watsi Da Tallafin Cedi Miliyan 20 Daga Kamfanin MTN
Sanarwar ta ce duk da cewa gwamnati ta yaba wa MTN Ghana kan wannan mataki da kuma kyakkyawar niyyarsa ta taimaka, ta yanke shawarar ƙin karɓar kuɗin saboda tuni ta ware isassun kuɗaɗe domin gudanar da aikin dawo da ’yan Ghana da ke cikin haɗari tare da taimaka musu wajen sake gina rayuwarsu bayan komawarsu gida.
Ma’aikatar ta ƙara da cewa Ministan Harkokin Wajen Ghana, Samuel Okudzeto Ablakwa, ya sanar da shugabannin hukumar gudanarwa da hukumar zartarwa ta MTN Ghana game da matsayar gwamnati tun ranar 14 ga Agusta, 2026.
Gwamnatin ta kuma tabbatar wa ’yan ƙasar cewa tana ci gaba da shirin dawo da dukkan ’yan Ghana da ke cikin yanayi na haɗari, tare da ɗaukar nauyin sake tsugunar da su da kuma taimaka musu wajen farfaɗo da rayuwarsu.
Bugu da ƙari, Ma’aikatar Harkokin Wajen ta yi alkawarin cewa bayan kammala aikin dawo da ’yan Ghana ɗin, za ta fitar da cikakken bayani kan kuɗaɗen da aka kashe domin tabbatar da gaskiya, riƙon amana da kuma yadda aka yi amfani da kuɗaɗen jama’a.
Gwamnatin Ghana ta kuma jaddada cewa ƙasar za ta ci gaba da kasancewa muhimmiyar cibiyar kasuwanci ga kamfanonin ƙasashen waje da ke gudanar da harkokinsu a Ghana, ba tare da la’akari da ƙasar da suka fito ba.
