News
Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Da Bullar Cutar Kwalara A Wasu Sassan Jihar
Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Kano (KNCDC) ta tabbatar da bullar cutar kwalara a wasu sassan jihar, yayin da adadin wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar ya kai 227.
Babban Daraktan hukumar, Farfesa Muhammad Adamu Abbas, ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar a Kano a wannan makon.
Sauron Da Jirgi Ya Dauko Daga Afirka Sun Yi Ajalin Mutane 2 A Jamus
Ya ce bayan hukumar ta samu rahoton bullar cutar, ta gudanar da bincike tare da tabbatar da kamuwa da cutar, inda aka bai wa wadanda suka kamu kulawar da ta dace.
A cewar daraktan, daga cikin mutane 227 da aka tabbatar sun kamu, 15 ne ke bukatar kulawa ta musamman, yayin da sauran ke ci gaba da samun kulawar lafiya da ta dace.
Hukumar ta kuma bukaci jama’a da su gaggauta kai duk wanda ya fara nuna alamomin amai da gudawa zuwa asibiti domin samun kulawa cikin gaggawa da kuma rage yiwuwar kara yaduwar cutar.
KNCDC ta ce daukar matakin gaggawa da neman magani da wuri na da muhimmanci wajen dakile yaduwar kwalara a tsakanin al’umma.
-
News3 days ago
Pantami Da Yaransa Sun Fantama Min Ƙarya, Domin Babu Inda Na Ba Shi Haƙuri, Inji Hajiya Naja’atu Muhammad
-
News1 day ago
Jami’an NSCDC Sun Cafke Mutane Biyu Da Saniyar Da Ake Zargin Ta Sata Ce A Kano
-
News2 days ago
Gwamnatin Kano Ta Ayyana 1 Ga Satumba A Matsayin Ranar Hutun Bikin Takutaha
