News
Hukumar EFCC ta gurfanar da wani mutum da laifin zamba a Abuja
Daga Yasir sani Abdullahi
Hukumar EFCC a ranar Litinin, 8 ga watan Agusta, 2022, ta gurfanar da wani mutum Mai suna Ahmed Umar a gaban mai shari’a A.O. Adeyemi Ajayi na babbar kotun birnin tarayya, Maitama Abuja, bisa tuhume-tuhume biyu na zamba da samun ta hanyar karya.
Wanda ake zargin ya gabatar da kansa a matsayin jami’in Flying Officer na rundunar sojojin saman Najeriya tare da karbar kudi N300, 000 daga hannun wani Caleb Ibrahim bisa zargin sama masa aiki.
Don cikakkun bayanai game da wannan da sauran labarai ku bibiya jaridar indaranka ( labaran gaskiya )
Advertisements
