Connect with us

News

Hukumar Kula da Shige-da-fice za ta ɗauki ma’aikata 5,000

Published

on

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Mukaddashin Kwanturola-Janar na Hukumar Kula da Shige-da-Fice ta Kasa, NIS, Idris Jere, ya ce ana shirin ɗaukar ƙarin ma’aikata 5,000 a hukumar.

Advertisement

Jere, wanda ya bayyana hakan a lokacin da yake amsa tambayoyi daga manema labarai a Dutse a jiya Asabar, ya ce matakin na da nufin magance matsalar karancin ma’aikata a hukumar ta NIS.

“Game da rashin isassun ma’aikata a NIS, kamar yadda kuka sani, yanzu mun kammala ɗaukar ma’aikata kuma muna horar da wadanda aka dauka a halin yanzu.

Advertisement

Kamar yadda kuka sani, gwamnati ta sanya takunkumin daukar ma’aikata, amma ta ɗage hakan a kan hukumomin tsaro, domin tsaro shine mafi muhimmanci.

“Don haka, mun rubuta wa shugaban ƙasa kuma na tabbata za mu samu amincewar ɗaukar karin ma’aikata kusan 5,000 a cikin NIS,” in ji Mista Jere.

Advertisement

Ya kara da cewa ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola, ya aike da takarda ga shugaban kasa Muhammadu Buhari, wanda ya nuna aniyar sa ta amincewa da bukatar ɗaukar ma’aikatan..

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Daily Nigerian

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending