Connect with us

News

Buhari na neman a tallafa wa ‘yan Pakistan da ambaliya ta ɗaiɗaita

Published

on

Muhammadu Buhari

DAGA YASIR SANI ABDULLAH 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana alhininsa game da ambaliyar ruwa “mafi tsanani” a tarihin ƙasar Pakistan, yana mai nema wa ƙasar tallafi daga hukumomin duniya.

 

Advertisement

Wata sanarwa daga Fadar Shugaban Ƙasa ta ce ambaliyar ta kashe mutum fiye da 1,000 tare da lalata gidaje da tituna da gadoji.

An kori sojojin da suka kashe Sheik Goni Aisami a aikin soja.

Advertisement

“Shugaba Buhari ya ce ‘yan Najeriya na ci gaba da taya ‘yan Pakistan da addu’a yayin da suke fuskantar wannan bala’i mai girman gaske,” a cewar Garba Shehu, mai magana da yawun shugaban ƙasa.

 

Advertisement

Buhari ya roƙi Majalisar Ɗinkin Duniya da sauran ƙungiyoyin agaji su taimaka wa “jama’ar da ruwa ya raba da muhallansu” da kuma “tallafa musu da abinci yayin da miliyoyi ke buƙatar agaji”.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending