News
Yajin Aiki: Ma’aikacin Jami’a Ya Kashe Kansa Saboda Kuncin Rayuwa
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADEEN
Wani ma’aikaci na Jami’ar Benin mai suna Carter Oshodin ya kashe kashe kansa a Jihar Edo saboda kuncin rayuwa.
Rahotanni sun bayyana cewa, ana zargin ma’aikacin ya yi wannan aika-aika ne sakamakon matsalar rashin kudi da ya rika fuskanta a bayan nan.
Wannan dai ya faru ne a daidai lokacin da Gwamnatin Tarayya ke ci gaba da haramta wa ma’aikatan jami’o’i albashinsu saboda yajin aikin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta ASUU.
Hukumar EFCC ta kama dan kasar China da ke hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a Kwara
Wakilinmu ya ruwaito cewa, gabanin faruwar lamarin, marigayi Carter wanda daya ne daga cikin wadanda yajin aikin ASUU ya shafa, ya rika koken kuncin rayuwa da har ta kai ga yana rokon makwabtansa taimakon kudi.
Wani daga cikin abokansa a shafin Facebook mai suna Edward, ya bayyana cewa marigayin ya shiga cikin matsananciyar damuwa musamman saboda yadda ya gaza biyan kudin makarantar ’ya’yansa mata biyu.
Tuni dai rundunar ’yan sandan Jihar Edo ta bakin mai magana da yawunta, Chidi Nwabuzor ta tabbatar da faruwar lamarin duk da a cewarta ba a shigar mata da rahoton faruwarsa ba a hukumance.
“Eh, tabbas mun samu labarin faruwar lamarin amma ba iyalan mamacin ne suka sanar da mu ba.
“Har ya zuwa yanzu babu wanda ya shigar mana da rahoton faruwar lamarin a hukumance, amma dai mun samu labari ta hanyar bibiyar abubuwan da ke faruwa a jihar.”
DAILY TRUST
-
News7 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News3 days agoKotu Ta Daure Wani Limamin Masallacin Juma’a Wata 1 Kan Tura Bidiyon Tsaraici Ga Matar Aure A Kano
-
News6 days agoƘalubalen Da Masu Ƙananan Sana’o’i Ke Fuskanta Saboda Ƙarancin Wutar Lantarki A Kano
