Connect with us

News

An Kama Matar Da Ta Kwaso Yara 9 Daga Kano Za Ta Kai Ogun

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Rundunar ’Yan Sandan jihar Kaduna ta ce ta kama wata mata a jihar da ta dauko yara tara a motar daukar kaya, daga karamar hukumar Danbatta da ke Kano, ta nufi jihar Ogun da su.

Advertisement

 

Yaran dai sun hada da masu shekaru 10 zuwa 15, kuma matar ta nufi garin Ijebu-Ode da je jihar Ogun ne da su, kafin a tare ta a jihar ta Kaduna.

Advertisement

Za A Kara Mafi Karancin Albashi Daga N30,000 —Ngige

 

Advertisement

Kakakin rundunar a Kaduna, DSP Muhammad Jalige, ya ce sun tare motar ce a shingen bincike na Kurmin Mashi, bayan sun lura babu taga ko daya a jikinta, duk da cewa akwai mutane a ciki.

 

Advertisement

“Da misalin karfe 4:00 na yammacin Lahadi ne jami’anmu suka kama motar.

 

Advertisement

“Daga matar har yaran ’yan Dambatta ne duka, kuma ta ce ta dauko su ne don taya ta sana’ar siyar da abinci da take yi a jihar Ogun.

 

Advertisement

“Amma ko hakan ma ta saba wa dokar kasa, saboda karancin shekarunsu,” inji Jalige.

 

Advertisement

Kakakin ya ce za su ci gaba da bincike kan lamarin, kafin daukar mataki na gaba.

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

AMINIYA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending