Connect with us

News

Gyaran Kundin Dokar Zaɓe: Majalisun Taraiya sun samu bambaci

Published

on

FB IMG 16426065479000562

Daga kabiru basiru fulatan

 

Advertisement

 

Majalisar Dattijai, a zaman ta na yau Laraba ta cire tsarin zaɓen fidda gwani na kai tsaye, wanda a ka fi sani da ƙato-bayan-ƙato.

Advertisement

Majalisar ta yi wa sashi na 84 kwaskwarima, in da ta maida shi cewa a zaɓen fidda gwani na jam’iya, za a iya yin ƙato-bayan-ƙato, ko naɗi, ko kuma yarjejeniya.

A tuna cewa a 2021 ne ta aikewa da Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari kundin gyaran dokar zaɓen, amma ya ƙi sanya hannu, in da ya ce sanya zaben ƙato-bayan-ƙato ya zama wajibi abu ne mai tsada, inda ya ƙara da cewa zai ɗorawa Nijeriya nauyi a tattalin arzikin ta da bai taka kara ya karya ba.

Advertisement

A ɗaya ɓangaren kuma, Majalisar Wakilai, a nata zaman na yau Laraba, ta sahale tsarin ƙato-bayan-ƙato da na naɗi, amma kuma ta cire tsarin yarjejeniya.

Sai dai kuma, da ga bisani sai ƴan majalisar su ka shiga ganawar sirri.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending