Connect with us

News

Buhari Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar Raya Yankin Neja Delta

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Shugaba Muhammadu Buhari ya nada Injiniya Emmanuel Audu-Ohwavborua a matsayin sabon mukaddashin Shugaban Hukumar Raya Yankin Neja Delta (NDDC).

 

Advertisement

Bayanin hakan ya bulla ne ta cikin wata sanarwa da NDDC ta fitar a Yammacin ranar Alhamis.

 

Advertisement

Ronaldo ba zai buga wa United wasa da Chelsea ba

Wannan dai na zuwa ne bayan da a safiyar wannan Alhamis din Shugaba Buhari ya kori Shugaban Hukumar, Mista Effiong Akwa,

Advertisement

 

“Biyo bayan amincewa da Shugaba Muhammad Buhari ya yi na korar Shugaban riko na Hukumar Raya Yankin NejaDelta daga mukaminsa, yanzu haka ya amince da mai biye masa a matsayi ya karbi ragamar gudanar da Hukumar.

Advertisement

 

“Zai ci gaba da rike matsayin ne har zuwa lokacin da za a nada wani sabon shugaban, tare da mambobin Kula da Harkokin Gudanarwar Hukumar,” a cewar sanarwar.

Advertisement

 

Kafin nada shi dai, Emmanuel ya kasance Babban Daraktan a hukumar, inda yanzu zai ci gaba da rike mukamin kafin a nada wani sabon shugaba da kuma mambobin gudanarwa na hukumar.

Advertisement

 

 

Advertisement

DAILY TRUST

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending