News
An Kai Hari 47 Kan Ofisoshin INEC A Shekara 3
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta kira taron tsaro na gaggawa kan yawaitar hare-haren da ake kai wa ofisoshinta a jihohi daban-daban.
INEC ta kira taron ne bayan harin da aka kai ofisoshinta na jihohin Ogun da Osun a ranar Alhamis, wadanda su ne na 47 da aka kai wa mata daga 2019 zuwa yanzu.
ASUU: Sanata Ndume ya ba da shawarar a zabtare albashin ‘yan majalisa a biya malaman Jami’a
’Yan Daba Sun kona Ofishin INEC na Ogun
INEC Ta Kama Ma’aikata 23 Masu Yi Wa Mutane Rajistar Bogi
Kwamishina Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a Kan Zabe an INEC, Festus Okoye, ya ce manya-manyan jami’an tsaro na hukumar ne za su halarci taron.
Ana sa ran Mai ba Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Tsaro za halarci zaman da zai gudana a hedikwatar INEC da ke Abuja a ranar Juma’a.
Taron zai tattauna ne kan yadda za a dakile hare-haren, la’akar da kusatowar babban zaben shekarar 2023.
Wata majiya a hukumar ta fada wa wakilinmu cewa da gangan ake kai wa hukumar hare-haren domin a gurgunta ayyukanta.
Wata majiyar ta daban kuma ta danganta hare-haren da masu fafutukar kafa kasar Yaarbawa ta Oduduwa.
“Sun kai hari kan wani wuri mallakin sojin Najeriya a Jihar Ogun kwanan nan, inda suka kwashi makamai” in ji majiyar.
-
News4 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News6 days agoKamfanonin Bada Bashi Ne Suka Cire N1.5bn Daga Albashin Ma’aikatan Kano — SSG
-
News5 days agoDr. Muhammed Musa Zango Ya Kaddamar Da Neman Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar APC
