Connect with us

News

An Kai Hari 47 Kan Ofisoshin INEC A Shekara 3

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta kira taron tsaro na gaggawa kan yawaitar hare-haren da ake kai wa ofisoshinta a jihohi daban-daban.

 

Advertisement

INEC ta kira taron ne bayan harin da aka kai ofisoshinta na jihohin Ogun da Osun a ranar Alhamis, wadanda su ne na 47 da aka kai wa mata daga 2019 zuwa yanzu.

ASUU: Sanata Ndume ya ba da shawarar a zabtare albashin ‘yan majalisa a biya malaman Jami’a

Advertisement

’Yan Daba Sun kona Ofishin INEC na Ogun

INEC Ta Kama Ma’aikata 23 Masu Yi Wa Mutane Rajistar Bogi

Advertisement

 

Kwamishina Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a Kan Zabe an INEC, Festus Okoye, ya ce manya-manyan jami’an tsaro na hukumar ne za su halarci taron.

Advertisement

 

Ana sa ran Mai ba Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Tsaro za halarci zaman da zai gudana a hedikwatar INEC da ke Abuja a ranar Juma’a.

Advertisement

 

Taron zai tattauna ne kan yadda za a dakile hare-haren, la’akar da kusatowar babban zaben shekarar 2023.

Advertisement

 

Wata majiya a hukumar ta fada wa wakilinmu cewa da gangan ake kai wa hukumar hare-haren domin a gurgunta ayyukanta.

Advertisement

 

Wata majiyar ta daban kuma ta danganta hare-haren da masu fafutukar kafa kasar Yaarbawa ta Oduduwa.

Advertisement

 

“Sun kai hari kan wani wuri mallakin sojin Najeriya a Jihar Ogun kwanan nan, inda suka kwashi makamai” in ji majiyar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending