Connect with us

News

ASUU: Sanata Ndume ya ba da shawarar a zabtare albashin ‘yan majalisa a biya malaman Jami’a

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Sanata Ali Ndume ya shawarci gwamnatin tarayya ta zabtare albashin ‘yan majalisa da kashi 50 cikin 100 domin biyan malaman jami’o’i da ke yajin aiki kuɗaɗensu.

 

Advertisement

Sanata Ndume da ke wakiltar Borno ta kudu a majalisar dattijai ya shaida hakan ne a birnin Maiduguri lokacin wani taro.

MATASAN KANO :Zasu iya biyan dubu biyar domin shan shayi – Kungiya

Advertisement

Jaridun Najeriya sun rawaito sanatan na cewa wannan abu ne da ya shafi kasa baki ɗaya, kuma dole a wasu lokutan a ɗau matakan ceto ‘yan kasa da ilimi.

 

Advertisement

Kiran da sanatan ya yi na zuwa ne adaida lokacin da malaman jami’i’oi ke korafin cewa rabin albashinsu aka basu bayan sun janye yajin aiki.

 

Advertisement

Dan majalisar dai na cewa lokaci ya yi da ya kamata a shawo kan matsalolin da ke durkusar da fanin ilimi a Najeriya.

 

Advertisement

A watan Oktoban da ya gabata ne, ASUU ta janye yajin aiki da ta shafe wata takwas tana yi ba tare da ta samu biyan bukatunta daga wajen gwamnatin tarayya ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending