Connect with us

News

Hatsarin mota ya ƙona mutum 11 ƙurmus a Jihar Kogi

Published

on

Wani tsohon hoto da ke nuna haɗari a kan hanyar Lokoja zuwa Abuja a watan Satumba

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Wani tsohon hoto da ke nuna haɗari a kan hanyar Lokoja zuwa Abuja a watan SatumbaImage caption: Wani tsohon hoto da ke nuna haɗari a kan hanyar Lokoja zuwa Abuja a watan Satumba

Mutum 11 sun ƙone ƙurmus a mummunan haɗarin mota da ya ritsa da ababe hawa daban-daban a yankin Ochadamu na Jihar Kogi da ke tsakiyar Najeriya.

Advertisement

An Kai Hari 47 Kan Ofisoshin INEC A Shekara 3

Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC) ta faɗa cikin wata sanarwa ranar Alhamis cewa hatsarin ya ritsa da ababen hawa 20.

Advertisement

 

Jami’in hulɗa da jama’a na FRSC, Bisi Kazeem, ya ce za a iya kare afkuwar haɗurran, yana mai kira ga masu ababen hawa da su dinga kula da abin hawan nasu akai-akai.

Advertisement

 

“Tawagar bincike ta ba da rahoton cewa lamarin ya ritsa da mutum 18,” in ji shi.

Advertisement

 

“Daga cikinsu, mutum bakwai – uku maza huɗu mata – sun ji raunuka daban-daban – yayin da sauran 11 ɗin waɗanda ba a iya tantance jinsinsu ba ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoton suka ƙone ƙurmus.”

Advertisement

 

Ya ƙara da cewa rahoton ya bayyana dalilin faruwar hatsarin da lalacewar titi, da shanyewar birki, da rashin ingancin abin hawa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending