Connect with us

News

Ficewar da ƴan Najeriya ke yi zuwa ƙasashen waje ba laifi ba ne – Adesina

Published

on

Femi Adesina

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan yaɗa labaru, Femi Adesina ya ce ba matsala ba ce ficewar da ƙwararru ke yi daga ƙasar zuwa ƙasashen waje domin neman aiki.

Advertisement

Amnesty na kira da a saki ɗalibin da a ka kama bisa suka ga Aisha Buhari

Adesina ya bayyana haka ne lokacin wata tattaunawa da kafar talabijin ta Channels cikin ƙarshen mako.

Ya ce bai kamata a ɗora wa gwamnatin shugaba Buhari laifin ficewar da da matasan ƙasar ke yi zuwa wasu ƙasashe domin neman aikin yi ba.

Advertisement

A cewar sa matasan na ficewa daga ƙasar tun kafin zuwan gwamnatin shugaba Buhari.

Masana dai na nuna damuwa kan yadda ƙwararru daga Najeriya, kamar likitoci, da masana kimiyyar yaɗa labaru da sadarwa ke tafiya ƙasashen waje saboda matsi na tattalin arziƙi da ake fama da shi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending