News
Ficewar da ƴan Najeriya ke yi zuwa ƙasashen waje ba laifi ba ne – Adesina
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan yaɗa labaru, Femi Adesina ya ce ba matsala ba ce ficewar da ƙwararru ke yi daga ƙasar zuwa ƙasashen waje domin neman aiki.
Amnesty na kira da a saki ɗalibin da a ka kama bisa suka ga Aisha Buhari
Adesina ya bayyana haka ne lokacin wata tattaunawa da kafar talabijin ta Channels cikin ƙarshen mako.
Ya ce bai kamata a ɗora wa gwamnatin shugaba Buhari laifin ficewar da da matasan ƙasar ke yi zuwa wasu ƙasashe domin neman aikin yi ba.
A cewar sa matasan na ficewa daga ƙasar tun kafin zuwan gwamnatin shugaba Buhari.
Masana dai na nuna damuwa kan yadda ƙwararru daga Najeriya, kamar likitoci, da masana kimiyyar yaɗa labaru da sadarwa ke tafiya ƙasashen waje saboda matsi na tattalin arziƙi da ake fama da shi.
-
Uncategorized7 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News6 days agoAƙalla Mutane 40 Sun Mutu Bayan Kifewar kwale-kwale A Sokoto
-
News2 days ago
Pantami Da Yaransa Sun Fantama Min Ƙarya, Domin Babu Inda Na Ba Shi Haƙuri, Inji Hajiya Naja’atu Muhammad
