News
Masu zanga-zanga sun toshe hanyoyi a arewacin Kosovo
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Masu zanga-zanga ‘yan Sabiya a arewacin Kosovo sun rufe tituna a rana ta biyu a ranar Lahadi bayan fafatawa da ‘yan sanda.
Manyan motocin dakon ƙaya ne suka toshe manyan tituna da ke kan iyaka da Sabiya.
An dade ana takun saka tsakanin hukumomi da ‘yan Sabiya marasa rinjaye a ‘yan makonnin nan.kamar yanda bbc hausa ta rawaito
Zanga-zangar ta baya-bayan nan dai ta samo asali ne sakamakon kama wani tsohon dan sandan Sabiya a ranar Asabar.
Firaministan kasar Albin Kurti, ya bayyana masu zanga-zangar a matsayin gungun masu aikata laifuka, inda ya kuma bukaci rundunar wanzar da zaman lafiya ta Nato a Kosovo da ta cire shingayen.
Kungiyar EU ta yi kira da a mai do da zaman lafiya, tana mai cewa wani makamin gurneti ya afkawa daya daga cikin motocinta masu sulke da ke sintiri a arewacin Kosovo a yammacin ranar Asabar.
‘Yan sandan Kosovo dai sun ce an yi musu luguden wuta a wurare daban-daban da ke kusa da wani tabki da ke kan iyaka da Sabiya a yammacin jiya Asabar, inda jami’ansu suka
