News
Kwamitin majalisar dattijai ya kira shugaban NNPC kan kwangilar naira biliyan 48
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Kwamitin da ke lura da ɗa’a da bin ƙa’ida da kuma sauraren korafe-korafe na majalisar dattijan Najeriya ya yi sammaci ga shugaban kamfanin mai na Malam Mele Kyari kan kwagilar bututun mai a yankin Neja Delta da takai naira biliyan 48.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa a 2022 ne Kamfanin NNPC ya bayar da kwangilar ga wani kamfani da ke da alaƙa da Ekpemupolo, da aka fi sani da Tompolo.
An yi tsammanin kamfanin zai gudanar da kwangilar naira biliyan hudu wadda za ta shafi Jihohin Delta da Ondo da Imo da Rivers da kuma wani ɓangare na jihar Bayelsa, tare da hadin gwiwar wasu masu ruwa da tsaki a yankin domin gudanar da aikin.
Kwamitin ya nemi shugaban kamfanin NNPC ya bayyana gabansa kan ƙorafin da al’umar Isoko suka shigar suna cewa ba a sanya matasansu ba cikin wannan kwagila ta biliyoyin naira.
