News
Kotu Ta Soke Zaben Adekele A Matsayin Gwamnan Osun
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Kotun sauraren kararrakin zaɓe ta ayyana Oyetola a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan Jihar Osun wanda aka gudanar a bara.
Alkalin kotun Mai Shari’a Tertsea Kume ita ta tabbatar da cewa tsohon gwamman ne ya ci zaɓen.
Bayan an bayar da hujja kan batun cewa an jefa ƙuri’un da suka wuce kima, an yanke hukunci kan cewa an saɓa doka wurin gudanar da zaɓen.
Tun da farko ɗan takarar gwamna a jam’iyyar APC Gboyega Oyetola ne ya shigar da ƙarar inda ya ƙalubalanci hukumar zabe mai zaman kanta INEC kan dalilin da ya sa ta bayyana ɗan takarar PDP Ademola Adeleke a matsayin wanda ya lashe zaɓe a watan Yulin 2022.
Advertisements
