Connect with us

News

Yarinyar Da Ta Bata A Kaduna An Gano Ta A Maiduguri

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

 

 

An gano wata yarinya mai shekara 13 a Maiduguri, babban birnin Jihar Borno, wadda ta bace kimanin makonni biyu da suka gabata a Jihar Kaduna.

 

Advertisement

Bayanai sun ce an gano yarinyar ce yayin da take sintiri a titi ba tare da sanin ina ta dosa ba, dalilin ke nan na kama ta kuma aka mika wa ’yan sandan yankin.

 

Dan Gwamnan Nasarawa Ya Riga Mu Gidan Gaskiya

Da yake jawabi yayin mika yarinyar ga iyayenta a ranar Alhamis, mai magana da yawun ’yan sandan Jihar Borno, ASP Sani Kamilu, ya ce sun yin bincike mai zurfi kafin gano iyayen yarinyar.

 

Ya ce, “Ta kasance karkashin kulawar CSP Hadiza Musa Sani wanda a ofishinta aka fara gabatar da batun mako biyu da suka shige.”

 

Advertisement

 

Mahaifin yarinyar, Ado Usman, ya ce wannan ba shi ne karon farko da ’yar tasa ke bacewa ba saboda rashin lafiya da take fama da ita.

 

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN), ya ce yarinyar ta kasa ba da bayani kan yadda aka yi ta tafi Maiduguri daga Kaduna.

 

(NAN)

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending