News
Kotu Ta Aike Da Shugaban EFCC Gidan Yari
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Babbar Kotun jihar Kogi ta ba da umarnin aikewa da Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta EFCC, Abdulrasheed Bawa, gidan gyaran hali saboda kin bin umarnin kotu.
Aminiya ta rawaito cewa Alkalin kotun, Mai Shari’a R.O. Ayoola ne ya bayar da umarnin a yayin zaman kotun na ranar Litinin.
Martani Shehu Sani Kan Hukuncin Kotun Koli, Da Ta Baiwa Lawan Tikitin Takara
Kotun ta kuma umarci Babban Sufeton ’Yan Sandan Najeriya, da ya kama tare da tsare Abdulrasheed din a gidan gyaran hali na Kuje har na tsawo kwana 14, har sai ya kare kansa daga zargin rashin da’ar.
Muna tafe da karin bayani…
Advertisements
