Connect with us

Sports

Napoli Na Shirin Lashe Serie A Karon Farko Cikin Shekara 33

Published

on

 

Kawo yanzu dai Napoli na bukatar maki 15 nan gaba domin ta lashe kofin babbar gasar tamaula ta Italiya a karon farko tun bayan 1990, wato shekaru 33 da suka gabata.

Advertisement

 

Napoli ta ci gaba da shirin lashe kofin Serie A na bana, bayan da ta je ta ci Torino 4-0 ranar Lahadi a wasan mako na 27.

Advertisement

 

BADGE  congratulated Bola Ahmad Tinubu for winning the presidential election.

Napoli ta fara cin kwallo minti tara da fara wasa ta hannun Victor Osimhen, sannan Khvicha Kvaratskhelia ya ci na biyu a bugun fenariti daga nan aka yi hutu.

Advertisement

 

Bayan da suka koma zagaye na biyu ne Osimhen ya kara na biyu kuma na uku a karawar, sannan Tanguy Ndombele ya ci na hudu.

Advertisement

 

 

Advertisement

Victor Osimhen, shi ne kan gaba a yawan cin kwallo a Serie A mai 21 a raga kawo yanzu, sannan mai biye da shi kuwa Lautaro Martinez ya ci wa Inter Milan 14.

 

Advertisement

Da wannan sakamakon Napoli ta ci wasa 10 a jere a fafatawa 11 a bayan nan a dukkan karawar da ta yi.

 

Advertisement

Torino ta ci kwallo a minti na 23, amma da alkalin wasa ya je ya duba a VAR sai ta fayyace cewar an taba da hannu kafin ta shiga raga, sai ya soke ta.

 

Advertisement

 

Ranar Lahadi Juventus ta je ta ci Inter Milan 1-0 a San Siro a dai gasar ta Serie A.

Advertisement

 

 

Advertisement

Wasan ya dauki zafi matuka inda aka bai wa dan kwallon Inter, Danilo D’Ambrosio da na Juventus, Leandro Paredes jan kati.

 

Advertisement

Bayan da aka ci Inter, kenan Lazio ta koma ta biyu a teburi, saboda ta ci abokiyar hamayyarta Roma 1-0.

 

Advertisement

An kuma kori dan kwallon Roma, Roger Ibanez, bayan da ya karbi katin gargadi guda biyu a wasan.

 

Advertisement

Mattia Zaccagni ne ya ci wa Lazio kwallon, wadda ta hada maki ukun da take bukata.

 

Advertisement

Daga baya alkalin wasan ya kara bayar da jan kati biyu bayan tashi a wasan, tun farko ’yan wasa sun kalubalanci juna da cacar baki da ta kai ya bai wa dan wasan Lazio, Adam Marusic da na Roma, Bryan Cristante jan kati.

 

Advertisement

Kungiyar Jose Mourinho ta barar da damar shiga gurbin zuwa Gasar Zakarun Turai ta Champions League, indq ta ci gaba da zama a mataki na biyar da tazarar maki daya tsakaninta da AC Milan ta hudu.

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending