News
Ƴan sanda na neman amaryar da ta yi harbi da bindiga lokacin bikinta
Ƴan sanda a jihar Uttar Pradesh da ke Indiya na neman wata amarya wadda ta harba bindiga a lokacin bikin aurenta.
Wani faifain bidiyo da aka wallafa a shafukan sada zumunta ya nuna yadda matar ta yi harbi sau huɗu a sama, lokacin da take zaune a kusa da angonta.
Tanzania za ta shirya musabaƙar Ƙur’ani da ƙasashe irin su ‘yan Najeriya
Ƴan sandan yankin sun ce amaryar ta yi ɓatan-dabo tun bayan faruwar lamarin.
Harba bindiga lokacin bukukuwan aure domin nuna murna a jihohin arewacin Indiya ba baƙon abu ba ne, sai dai yakan haifar da asarar rayuka a lokuta da dama.
A shekara ta 2016 wata kotu a jihar ta Uttar Pradesh ta buƙaci a rinƙa yin bincike kan duk wani bikin aure da aka harba bindiga.
Wani ɗan’uwan amaryar ne ya naɗi bidiyon harba bindigar sannan ya watsa shi a shafin sada zumunta.
-
News4 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News6 days agoKamfanonin Bada Bashi Ne Suka Cire N1.5bn Daga Albashin Ma’aikatan Kano — SSG
-
News5 days agoDr. Muhammed Musa Zango Ya Kaddamar Da Neman Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar APC
