Connect with us

News

Tsohon shugaban ƙasa Umaru Musa Yar’adua ke cika shekaru 13 da rasuwa 

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

A yau ne tsohon shugaban ƙasar Nigeria marigayi Alhaji Umaru Musa Yar’adua ke cika shekaru 13 da rasuwa.

 

Advertisement

Umaru Musa Yar’adua ya rasu ne a ranar 5 ga watan Mayu shekarar 2010 a fadar Asorok dake Abuja bayan ya dawo daga dogon jinya a ƙasashen waje, inda mataimakinsa Dr. Goodluck Jonathan ya maye gurbinsa.

Kamfanin jirgin sama na Rano Air ya sanar da ranar fara zirga-zirga.

Umaru Musa Yar’adua ya mulki Nigeria tsakanin ranar 29 ga watan Mayu shekarar 2007 zuwa ranar 5 ga watan Mayu shekarar 2010

Advertisement

 

Shine ya lashe zaɓen shugaban ƙasa da aka gudanar a ranar 21 ga watan Afrilun shekarar 2007, inda ya kada abokan takararsa Irin su Muhammadu Buhari na jam’iyyar ANPP da ATIKU ABUBAKAR na jam’iyyar ACN.

Advertisement

 

An haifeshi a ranar 16 ga watan Agusta shekarar 1951 a garin Katsina. Ya kuma halarci kwalejin Barewa da Jami’ar Ahmadu Bello duk a birnin Zaria dake jihar Kaduna.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending