Connect with us

News

Gwamna Jahar Edo Ya Fitar Da Ofishin Mataimakinsa Daga Gidan Gwamnati

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.

 

Da alama rikicin da ake fama da shi tsakanin Gwamnan Edo, Godwin Obaseki da Mataimakinsa, Philip Shaibu, ya dauki sabon salo bayan an mayar da ofishin mataimakin wajen gidan gwamnatin Jihar.

Bayanai sun nuna ofishin, wanda a baya yake cikin gidan gwamnatin a Benin City babban birnin Jihar, a yanzu an mayar da shi wani gini da ke kan titin Dennis Osadebey a cikin birnin.

Man Fetur Zai Sauko Zuwa Ƙasa Da N200 a Kowace Lita Idan Aka Gyara Matatu, -IPMAN

Tuni dai aka kafa allon da ke dauke da rubutun “Ofishin Mataimakin Gwamna” a mashigar ginin.

Da aka tuntube shi, Kwamishinan Sadarwa da Wayar da Kan Jama’a na Jihar, Chris Nehikare, ya ce, “Idan dai ta tabbata akwai allon a kafe a wajen, to haka ne ke nan.”

Advertisement

Rikici tsakanin mutanen biyu dai ya fara ne a kan yunkurin Philip na neman kujerar lamba daya a jihar, matakin bisa ga dukkan alamu Obaseki bai yi na’am da shi ba.

Philip dai ya fito ne daga yankin Arewacin Edo, na neman ya gaji Obaseki ne, wanda ya fito daga Kudancin Edo, amma shi kuma ya fi son wani daga Edo ta Tsakiya.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending