News
Jirage Zasu Rika Biyan Diyya Ga Fasinjojin Da Suka Yi Jinkirin Tashi -Ministan sufurin jiragen sama
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo, Ya ce hukumomi dake kula da harkokin sufurin jiragen sama a kasar nan zasu fara tilastawa kanfanonin jiragen sama biyan diyya ga fasinjojin da suka fuskanci tsaikon tashin jirginsu, ko kuma aka soke tashin jirgin baki dayansa, daga watan janairun sabuwar shekara ta 2024.
Ministan ya baiyana haka ne a lokacin da ya baiyana gaban hadakar kwamitin kula da sufurin jiragen sama na zaurikan majalisun dokokin kasa, domin kare kudirin kasafin kudin ma’aikatarsa.
Matashi ya kashe kansa bayan ya yi asarar Naira miliyan 2.5 a cacar yanar gizo
Ya ce za’a yi ragin kudin tikiti ga fasinjojin da suka fuskanci tsaikon tashin jirginsu a wani bangare na biyansu diyya.
Ministan ya kuma bada tabbacin cewar za’a rika wallafa sunayen jiragen da suka yi jirgin tashin fasinjojinsu a kafafen yada labarai a kowane mako.
A wani labarin kuma Matashi ya kashe kansa bayan ya yi asarar Naira miliyan 2.5 a cacar yanar gizo
Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.
Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.
A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.
Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
