News
Shugaba Tinubu ya dakatar da ministar jin ƙai Betta Edu nan take
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya dakatar da ministar jin ƙai, Betta Edu nan take.
Kakakin shugaban Najeriyar, Ajuri Ngelale ne ya sanar da matakin dakatar da ministar jinkan ta cikin wata sanarwa da aka fitar a yau.
Shugaba Tinubu ya ɗauki matakin ne domin ba da dama ga hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa ta gudanar da bincike a kanta.
Tun farko al’ummar Najeriya sun yi ta matsin lamba akan sai an Dakar da ita inda suke kiraye-kiraye GA gwamnatin tarayya data dakatar da ita daga mukaminta domin a gudanar da cikakken bincike a kanta game da zarge-zargen da ake mata.
Ana zargin ta da bayar da umarnin tura kuɗi kimanin naira miliyan 585 zuwa asusun bankin wata mata kamar yanda kafafen yada labarai da dama suka rawaito
