News
Ma’aikatan Lafiya Sun Tsinduma Yajin Aikin Gargadi A Kaduna
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Ma’aikatan lafiya a jihar Kaduna sun shiga yajin aikin gargadi na kwanaki biyar.
Binciken da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN ta yi a wasu asibitocin gwamnati ya nuna cewa likitoci da ma’aikatan dakin gwaje-gwaje ne kawai ke bakin aiki.
Shugaba Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Ɓude Iyakokin Nijeriya Domin Shigo Da Wasu Kayayyakin Abinci.
Sakamakon haka ne ya sa, aka sallami da yawa daga cikin majinyatan da ke asibitocin saboda babu masu kula da su.
Da yake jawwbi a wata hira da aka yi da shi ranar Litinin a Kaduna, Shugaban ƙungiyar ma’aikatan jinya da ungozoma ta kasa a jihar, Mista Ishaku Yakubu, ya ce sun shiga Yajin aikin ne domin biyan wasu bukatun da suke nema a biya musu.
Ya ƙara da cewa akwai bukatu da aka mikawa gwamnatin jihar tsawon shekaru amma har yanzu basu ce komai ba.
Yakubu ya ce, “Ma’aikatan lafiya sun fara yajin aikin ne a kan batutuwan da har yanzu gwamnati ta ƙasa tsaida matsaya.
Ya ƙara da cewa har yanzu gwamnatin jihar ba ta fara biyan mualawus alawus ɗin da gwamnatin tarayya ta kaddamar ba tun shekarar 2003 .
Da aka tuntubi babbar sakatariyar ma’aikatar lafiya ta jihar, Dakta Aishatu Mohamed-Saqid, ta ce za ce wani abu a hukumance dangane da wannan lamari.
-
News6 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News2 days ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News7 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
