Connect with us

Sports

Da Ɗumi-Ɗumi: Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Ta Naɗa Sabon Koci  

Published

on

Advertisements
ads

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, ta naɗa Abdullahi Usman a matsayin sabon mai horar da ƴan wasanta.

Ƙungiyar wacce ta lashe gasar frimiyar Nijeriya sau huɗu, ta sanar da hakan ne a shafinta na ‘Facebook’.

Da Ɗumi-Ɗumi: Gwamnatin Borno Ta Yi Kwaskwarima Wa Dokar Hana Fita

Ta ce “Mu na farin cikin sanar da cewa mun cimma yarjejeniyar naɗa Usman Abdullahi a matsayin sabon kocinmu.”

Ƙwararren kocin ya yi aiki da manyan ƙungiyoyi a frimiyar Nijeriya da su ka haɗa da; Enyimba da Wikki Tourists.

Hakan nan, tsohon Mataimakin kocin Super Eagles ɗin ya taimaka wa Katsina United wajen haurowa gasar frimiyar shekaru biyu da su ka gabata.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending