Connect with us

News

Daurarru Na Mutuwa Saboda Yunwa A Gidajen Yarin Najeriya 

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Hukumar dake lura da gidan ajiya da gyaran hali ta Calabar dake jihar cross river ta ce ta na bincike kan matsalar ciyar da daurarru dake ajje a gidan domin tabbatar da walwalar su.

Advertisement

Kakakin hukumar na jihar Abubakar Umar ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da kamfanin dillanci labarai na Nijeriya NAN a birnin Abuja ranar talata.

Ko Wanne Mataki Kungiyoyin Kwadago Zasu Dauka Kan Karin Man Fetur A Najeriya 

Inda yace ministan cikin gida na Olubunmi Tunji-Ojo, ya bayar da umarnin a gudanar da bincike kan zargin badakala a harkokin ciyar da daurarru a gidan ajiya da gyaran hali na Afokang dake tsakiyar Calabar a jihar Cross River.

Advertisement

Umarnin na zuwa ne bayan wani faifan bidiyo daya fito kan yadda ake lura da daurarrun, wanda ciki harda yadda ake basu wani wake da bai dahu ba a lokacin Karin kumallo.

Ko dai ta cikin wani sako da Dan jarida Ja’afar Ja’afar Ya wallafa a shafinsa na facebook ya bayyana yadda wani ma’aikacin gidan gyaran hali da tarbiyya ya aike masa da wani sako kan halin da daurarru ke ciki a gidan ajiya da gyaran hali.

Advertisement

Sakon yace “Sir mutane na mutuwa a Prison saboda yunwa” “Wallahi a inda nake aiki kullum sai an fita da gawa” “kuma Yunwa ce”.

“sun hana kowa shiga da Phone (waya) don kada a dauki hoton abinci”

Advertisement

“hoton dake yawo na calaba Prison to kusan duk sauran prison din haka suke babu abinci”

“Staff wani lokacin ke taimakon Inmate da abinci da ga cikin salary su” “wallahi ko ni kusan duk sati sai na sayi kuli-kuli da garin rogo na rabawa inmate”.

Advertisement

 

PRNIGERIA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending