News
Yan Sanda Sun Kama Angon Bisa Zarginsa Da Hallaka Amaryarsa Har Lahira.
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Rundunar ‘yan sanda a jihar Legas ta ce ta kama wani Ango dan shekara 30, mai sunan Motunrayo Olaniyi, bisa zarginsa da daba wa matarsa mai suna Olajumoke ‘yar shekara 25 daba mata wuka har lahira.
Kakakin rundunar ‘yan sandan,jihar SP Benjamin Hundeyin, ya tabbatar da faruwar lamarin ga Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ranar Asabar a Jihar.
Ya ce lamarin ya faru ne a ranar Juma’a da misalin karfe 1:00 na rana a Amazing Grace Estate, Elepe, a yankin Ikorodu na jihar.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
