News
Hukumar FCDA Ta Yi Barazanar Kwace Wasu Filaye Mallakar ‘Ya’yan Buhari Da Wasu Manyan Ƙasa A Najeriya
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Hukumar da ke kula da babban birnin tarayya Abuja ta hannun hukumar raya babban birnin tarayya FCDA, ta yi barazanar ga wasu fitattun ‘yan Najeriya da suka haɗa da ‘ya’yan tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, Yusuf da Zahra, da su biya kuɗaɗen da ake bin su na filaye a cikin kwanaki 14, ko kuma su rasa haƙƙin mallakar Filaye.
PREMIUM TIMES ta ruwaito cewa ana sanar da duk wanda abin ya shafa cewa rashin biyan duk wasu kuɗaɗen filaye da kuma caji a cikin lokacin da aka ƙayyade zai haifar da janye tayin mallaka (R-of-O) akan filayen da aka ambata.
Haka zalika Hukumar tà yi barazanar janye haƙƙin mallakar filayen da fitattun ‘yan Najeriya suka mallaka idan har suka kasa biyan kuɗaɗensu cikin kwanaki 14.
Mutanen da abin ya shafa sun haɗa da:
– Femi Gbajabiamila, shugaban ma’aikatan shugaban ƙasa Bola Tinubu
– Abbas Tajudeen, kakakin Majalisar wakilai
– George Akume, Sakataren Gwamnatin Tarayya
– Olubunmi Tunji-Ojo, Ministan Harkokin Cikin Gida
– Bukola Saraki, tsohon shugaban Majalisar Dattawa
– Yakubu Dogara, tsohon kakakin Majalisar Wakilai
– Ovie Omo-Agege, tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa
– Theodore Orji, Rochas Okorocha da Ibikunle Amosun, tsoffin gwamnoni
– Dino Melaye, Kabiru Marafa, Stella Oduah, da Ben Bruce, tsaffin ‘yan majalisa
– Adamu Abdullahi, tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa
– Ameh Ebute, Shugaban Majalisar Dattawan Jamhuriyya ta uku
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
