Connect with us

News

Wasu ‘Yan Kasuwa Sun Koka Kan Halin Da Suke Ciki Na Yunkurin Sabunta Kasuwar Mile 12

Published

on

Wasu 'yan Kasuwa sun koka kan halin da suke ciki na yunkurin Sabunta Kasuwar Mile 12 dake Jihar Lagos

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

Wasu Yan Kasuwar Mile 12 dake Jihar Lagos da suka fito daga Jihohin Arewa Dan sauran sassan Najeriya sun koka da halin da suka samu kansu a Kasuwar Mile 12 dake Jihar Lagos.

Advertisement

Sun zargi cewa Gwamnatin Jihar Lagos a yunkurinta na sabunta Kasuwar ta samar da wani Dan Kwangila da zai aikin, sannan Yan Kasuwar zasu sake biyan wasu kudade gareshi duk da cewa Shagunan Mallakinsu ne da suka siya daga Gwamnati tun Asali Kamar yanda Arewa Radiyo ta ruwaito.

Yawan Shan Sukari Ga Kananan Yara Na Haifar Da Cutar Suga Idan Aka Girma —Bincike

Yan Kasuwar sun bukaci Gwamnatin data Basu tabbacin ba tashinsu zasuyi daga Kasuwar ba bayan an gama Sabuntata. Tare da bukatar da Manyan Kasuwar ta Mile 12 da suyi musu cikakken bayani kan yadda ake tasrifi da kudin shiga na Kasuwar da aka dade ana Tarawa.

Advertisement

Sun bayyana cewa kudaden da akasa kan kowanne Shago da za a sake ginawa ya kai kimanin Naira Miliyan 5 Wanda hakan kuma yayi musu tsada a cewar wasu ‘yan Kasuwar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending