News
Gobara Ta Kone Kasuwar Katako A Legas
DAGA NUSIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA
Gobara ta kone wata kasuwar unguwar Ebute Metta da ke jihar Legas.
Jami’an Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Legas da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Legas na shirin kai daukin a wajan da lamarin gobarar da ta tashi a kasuwar Oko Baba.
DA DUMI-DUMI: Hukumar DSS Sun Chafke Shugaban Jaridar Sahara Reporters Bayan Isowarsa Najeriya
Wani mai amfani da shafin X, Adedeji Olalekan, ya ce gobara ta shafi rumfunan kasuwar kamar yanda jaridar Daily Post ta ruwaito.
“Titin Okobaba yana cin wuta a yanzu, duk wuraren da ake amfani da su na konewa,” ya wallafa a shafinsa na Twitter.
Advertisements
