News
DA DUMI-DUMI: Hukumar DSS Sun Chafke Shugaban Jaridar Sahara Reporters Bayan Isowarsa Najeriya
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Jami’an Hukumar DSS sun kama Omoyele Sowore, jagoran kungiyar #RevolutionNow Movement da ke adawa da gwamnati a filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ke Legas.
Jami’an sun tsare Sowore, mawallafi jaridar yanar gizo ta Sahara Reporters a yau Lahadi jim kaɗan bayan ya sauka a filin jirgin saman.
Ana Fargabar Mutuwar Mutane 64 Bayan Kifewar Kwale-kwale A Zamfara
Kafin saukar sa, wasu ƙungiyoyin gwagwarmaya sun yi wa filin jirgin saman tsinke domin tarbar sa yayin da ya ke dawowa daga Amurka shi da iyalin sa.
Rahotanni sun baiyana cewa tun ranar Alhamis a ka fitar da bayanin umarnin kama Sowore idan ya dawo kasar, inda ya yi alla-wadai da hakan ya kuma jaddada aniyarsa ta dawowa Nijeriya.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
