Connect with us

News

Ana Fargabar Mutuwar Mutane 64 Bayan Kifewar Kwale-kwale A Zamfara

Published

on

kwale kwale

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

Ana fargabar mutuwar mutane 64 bayan kifewar kwale-kwale da suke ciki ranar Asabar a karamar hukumar Gummi ta jihar Zamfara dake Najeriya, kasancewar mutane 6 kacal aka samu damar cetowa daga cikin 70 din da suka dulmiye a cikin ruwan.

Advertisement

Shugaban karamar hukumar ta Gummi Aminu Nuhu Falale, ya ce kwale-kwale na dauke da manoma 70, a kan hanyarsu ta zuwa gonakinsu da safiyar Asabar, to amma ma’aikatan agaji sun samu nasarar zakulo 6 a raye, sannan kuma suna ci gaba laluben sauran wadanda suka nutse a cikin ruwan.

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Gargaɗin Sake Samun Mummunar Ambaliyar Ruwa A Jihohin Najeriya Biyu

Kimanin kusan manoma dubu daya ne ke jigilar zuwa gonakinsu ta wannan yanki a kullum rana, to amma kwale-kwale ruwan guda biyu ne kacal suke amfani da su domin wannan zirga-zirga, lamarin da ke janyo cikar jiragen ruwan fiye da kima a duk lokacin da suke tafiyar, kamar yadda wani mai rike da sarautar gargajiya na yankin ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters.

Advertisement

 

 

Advertisement

DW

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending