Connect with us

News

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Gargaɗin Sake Samun Mummunar Ambaliyar Ruwa A Jihohin Najeriya Biyu

Published

on

Mutum 259 ne suka mutu yayin da 625,239 suka rasa matsugunansu a ambaliyar ruwa a Nijeriya – NEMA

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

Ministan Albarkatun ruwa da tsaftar muhallai a  Najeriya, Joseph Utsev ya yi gargaɗin sake samun mummunar ambaliyar Ruwa a kogunan Neja da Benue.

Advertisement

Yayin da yake jawabi ga taron menama labarai a Abuja, Ministan ya ce an samu ƙaruwar ruwan da ke ƙwarara a kogunan biyu zuwa yankin Naija Delta da ke kudancin Najeriya.

Yadda CBN Ya Ƙaƙaba Wa Masu POS Ƙa’idoji Da Dabaibayin Yin Hada-hadar Kuɗaɗe

‘A yayin da muke jajanta wa al’ummomin jihohin Borno da Yobe da Jigawa da Bauchi da sauran jihohin da suka fuskanci ambaliyar Ruwa, muna ƙara jan hankalin ‘yan ƙasar game da yiwuwar sake fuskantar wata ambaliyar daga kogunan Benue da Neja da wasu yankunan yankin”, in ji ministan.

Advertisement

Kan haka ne mista Utsev ya yi kira ga mazauna yankin su ɗauki matakai domin kauce wa bala’in ambaliya a wasu sassan kudancin ƙasar.

Gargaɗin na zuwa ne a daidai lokacin da al’ummar birnin Maiduguri ke fuskantar mummunar ambaliya da ta auka wa birnin sakamakon fashewar madatsar ruwa ta Alau da ke wajen birnin.

Advertisement

PRNIGERIAN ta ruwaito cewa Gwamnan jihar Babagana Umara Zulum ya ce lamarin ya shafi kusan mutum miliyan biyu.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending