News
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Gargaɗin Sake Samun Mummunar Ambaliyar Ruwa A Jihohin Najeriya Biyu
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Ministan Albarkatun ruwa da tsaftar muhallai a Najeriya, Joseph Utsev ya yi gargaɗin sake samun mummunar ambaliyar Ruwa a kogunan Neja da Benue.
Yayin da yake jawabi ga taron menama labarai a Abuja, Ministan ya ce an samu ƙaruwar ruwan da ke ƙwarara a kogunan biyu zuwa yankin Naija Delta da ke kudancin Najeriya.
Yadda CBN Ya Ƙaƙaba Wa Masu POS Ƙa’idoji Da Dabaibayin Yin Hada-hadar Kuɗaɗe
‘A yayin da muke jajanta wa al’ummomin jihohin Borno da Yobe da Jigawa da Bauchi da sauran jihohin da suka fuskanci ambaliyar Ruwa, muna ƙara jan hankalin ‘yan ƙasar game da yiwuwar sake fuskantar wata ambaliyar daga kogunan Benue da Neja da wasu yankunan yankin”, in ji ministan.
Kan haka ne mista Utsev ya yi kira ga mazauna yankin su ɗauki matakai domin kauce wa bala’in ambaliya a wasu sassan kudancin ƙasar.
Gargaɗin na zuwa ne a daidai lokacin da al’ummar birnin Maiduguri ke fuskantar mummunar ambaliya da ta auka wa birnin sakamakon fashewar madatsar ruwa ta Alau da ke wajen birnin.
PRNIGERIAN ta ruwaito cewa Gwamnan jihar Babagana Umara Zulum ya ce lamarin ya shafi kusan mutum miliyan biyu.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
