News
Ambaliyar Ruwa Ta Hallaka Mutane Biyu, Ta Raba Iyalai Da Muhallansu A Damaturu
Akalla mutum biyu sun rasa rayukansu sakamakon mummunar ambaliyar ruwa da ta afku a birnin Damaturu, babban birnin Jihar Yobe, bayan ruwan sama mai ƙarfi da aka yi a ranar Lahadi.
Lamarin ya shafi unguwannin Malari, Pompomari da wasu yankunan da ke makwabtaka da su, inda ambaliyar ta mamaye gidaje da hanyoyi, tare da tilasta wa wasu mazauna barin muhallansu domin tsira.
’Yan Bindiga Sun Sace Tawagar Rakiyar Amarya Daga Katsina Zuwa Kebbi
Rahoton gaggawa da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Yobe (SEMA) ta fitar ya tabbatar da cewa mutum biyu ne suka mutu a wannan ibtila’i.
Hukumar ta bayyana sunayen mamatan da Isa Haruna, mai shekaru 38 kuma jami’in tsaro, da Abba Kyari mai shekaru 18, wanda ya nutse a yankin Pompomari.
SEMA ta ce tawagarta ta neman ceto ta haɗa kai da jami’an Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Yobe bayan samun kiran gaggawa daga al’ummomin da ambaliyar ta shafa.
A cewar hukumar, bayan isa wurin da lamarin ya faru, an tabbatar da rasuwar mutanen biyu, sannan aka kai gawarwakinsu zuwa ɗakin ajiyar gawa na Asibitin Kwararru na Janar Sani Abacha da ke Damaturu.
Ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, gwamnatin jihar ba ta bayyana adadin gidaje ko kadarorin da ambaliyar ta lalata ba.
-
News6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Umarci Masu Talla Da Masu Sana’ar Jari Bola Su Bar Karkashin Gadar Tal’udu
-
News2 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News3 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
