News
DSS Sun Kubutar Da Sakataren Karamar Hukumar Da Aka Yi Garkuwa Da Shi A Kano
Hukumar tsaron farin kaya ta DSS a Najeriya ta sanar da kubutar da Sakataren Mulki na Karamar Hukumar Kibiya da ke Jihar Kano, Hon. Hamza Musa Durba, bayan da aka yi garkuwa da shi.
A cewar rahotanni, jami’an tsaron sun gudanar da wani samame a wani daji da ke yankin Kibiya, inda suka samu nasarar ceto jami’in gwamnati ba tare da ya samu wata illa ba.
Ƴan Kasuwa Sun Ƙi Sauko Da Farashin Mai Duk Da Raguwar Sa A Kasuwar Duniya
Majiyoyi sun bayyana cewa jami’an sun fara tattaunawa da wadanda suka yi garkuwa da shi ta wayar tarho, lamarin da ya taimaka musu wajen gano maboyar wadanda ake zargin.
Rahoton ya kara da cewa jami’an DSS sun kama mutane biyu daga cikin wadanda ake zargi, inda aka same su da bindiga kirar AK-47.
A halin yanzu, hukumomin tsaro sun ce ana ci gaba da bincike domin gano sauran wadanda ke da hannu a lamarin.
DAILY NIGERIAN
-
News1 day ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
-
News2 days ago
Ana Zargin Matar Aure Da Shaƙe ’Yar Kishiyarta Mai Shekara 3 Har Lahira
-
News6 days ago
KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli
