News
Jami’ar Al-Istiqama Ta Sanar da Ranar Bikin Yaye Dalibai Na 2025 A Yayin Da Makarantar Ke Daukar Matakan Inganta Ilimi
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Jami’ar Al-Istiqama da ke Sumaila na farin cikin sanar da bikin yaye dalibanta, wanda za a gudanar daga ranar 21 zuwa 22 ga Fabrairu, 2025. Wannan muhimmin taro zai zama damar murnar nasarorin da daliban jami’ar suka cimma, tare da jaddada aniyar jami’ar na ci gaba da samar da ingantattun hanyoyin karatu da jin daɗin dalibai.
Jami’ar Al-Istiqama, wacce ke da matsuguni a wajen birnin Kano, na bai wa dalibai damar mayar da hankali kan karatunsu ba tare da wata tangarda ba. Wannan yanayi mai natsuwa da cike da kwanciyar hankali yana taimakawa wajen haɓaka hazakar ɗalibai da haɓaka ɗabi’a mai kyau.
Ba Za Mu Zuba Ido Muna Ganin Malamai Na Cutar Da ‘Dalibai Ba -Gwamna Yusuf
Manyan Sauye-Sauyen da Jami’a Ke Aiwtarwa
A halin yanzu, jami’ar na aiwatar da gagarumin gyare-gyare da ci gaba don ƙarfafa harkokin ilimi da jin daɗin dalibai. Daga cikin manyan ayyukan da ake aiwatarwa sun haɗa da:
Shinfida sabbin tituna a cikin harabar jami’a tare da saka fitilun hasken rana don tabbatar da tsaro da kyakkyawan yanayi.
Inganta gine-ginen jami’a da samar da kayan aiki na zamani a dakunan karatu, azuzuwa, da dakunan gwaje-gwaje domin bai wa malamai da dalibai damar gudanar da karatu da bincike cikin sauƙi.
Sabunta gidajen kwanan dalibai don samar da matsuguni mai kyau da tsari ga ɗalibai maza da mata.
Ƙarfafa tsarin samar da wutar lantarki, inda ake haɗa wutar grid, janareta, da makamashin hasken rana don samar da wuta mara yankewa.
Jami’a Mai Da Muhimmanci Ga Ilimi da Tarbiyya
Sanata Abdurrahman Kawu Sumaila, wanda ya kafa jami’ar kuma ke jagoranta, ya bayyana cewa waɗannan sauye-sauyen suna daga cikin shirinsa na ganin jami’ar ta zama jagaba a fannin ilimi da bincike a matakin duniya. Ya ce:
“Burina shi ne samar da haɗin gwiwa tsakanin ilimi da tarbiyya, musamman a Arewacin Najeriya. Jami’ar mu tana samar da yanayi mai daɗi ga dalibai don su samu ilimi mai inganci tare da kyakkyawan ɗabi’a. Mun kuduri aniyar ci gaba da inganta ingancin karatu da kuma kafa muhalli mai tsari da goyon baya ga dalibai.”
Daya daga cikin ginshikan Jami’ar Al-Istiqama shi ne tabbatar da tsaro da ɗa’a. Jami’ar na da tsauraran matakai kan hana amfani da miyagun ƙwayoyi, don tabbatar da cewa dalibai da malamai suna cikin ingantaccen yanayi mai lafiya da kwanciyar hankali. Ta hanyar haɗin gwiwa da hukumomin tsaro, jami’ar ta kafa kanta a matsayin ɗaya daga cikin manyan cibiyoyin ilimi mafi aminci a Jihar Kano.
Jami’a Mai Manufar Ilimi da Cigaban Zamani
Tun daga kafuwarta, Jami’ar Al-Istiqama ta himmatu wajen cike giɓin ilimi, samar da damar karatu na ƙasa da ƙasa, da bunƙasa bincike da ƙirƙire-ƙirƙire a cikin tsoron Allah. Wannan tsari na haɗa ilimi da kyawawan dabi’u, tare da sauƙin farashi da ci gaba a fannin fasaha da kare muhalli, ya sa jami’ar zama ɗaya daga cikin manyan cibiyoyin ilimi masu tasiri a Najeriya da ma duniya baki ɗaya.
A yayin da jami’ar ke shirin gudanar da bikin yaye dalibai a Fabrairu 2025, tana maraba da sabbin dalibai, iyaye, da duk masu ruwa da tsaki don su shaida wannan sabon babi a tarihin jami’ar.
-
News4 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News6 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
