Connect with us

News

Ba Za Mu Zuba Ido Muna Ganin Malamai Na Cutar Da ‘Dalibai Ba -Gwamna Yusuf

Published

on

Gwamnan Kano Abba Kabir Ya Yi Tafiya, Yayin Da Rikici Ke Ƙara Tsamari A Jami’yyar NNPP A Kano

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

Gwamnan jihar Kano, Alhaji  Abba Yusuf ya yi gargadi ga malaman makarantu da kada su umurci dalibai yin ayyuka masu tsauri a ciki ko wajen makaranta.

Advertisement

Hakan na kunsha ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ga manema labarai.

Gwamnan ya jaddada cewa makarantu wajen ba da ilimi ne da jagoranci, kyautata ɗabi’a ba wajen bautar da dalibai ba.

Advertisement

Wannan mataki ya biyo bayan wata ziyarar bazata da gwamnan ya kai wata makarantar koyar da larabci da ke Kano, inda ya tarar da dalibai su na aiki mai wahala a cikin makarantar .

A bayyane gwamnan ya nuna rashin jin daɗi, tare da tambayar shugaban makarantar game da sanya dalibai irin waɗannan ayyuka.

Advertisement

Haka zalika ya ce tabbas gwamnatinsa ba zata zuba ido taga ana cutar da Yan makaranta ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending