Connect with us

News

Kungiyar Yan Jaridu Ta Yabawa Dan Majalisa Rurum Bisa Tallafawa ‘Ya’yanta A Lokacin Azumin Ramadana

Published

on

1000273473

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Kungiyar ‘Yan Jarida da Masu Buga Labarai a yanar gizo ta  Northern Online Media Group  (NORP), reshen Jihar Kano, ta jinjinawa wakilin mazabar Rano, Kibiya, da Bunkure a Majalisar Tarayya, Hon. Kabiru Alhassan Rurum, saboda Kyautatawar tallafin buhunan shinkafa na kilogiram 25 da ya bai wa kowane memba a matsayin kyautar Ramadan.

Advertisement

A cikin wata sanarwa da shugaban rikon kwarya na kungiyar, Comrade Abbas Yusha’u Yusuf, ya sanya wa hannu, NORP ta bayyana cewa wannan kyauta wata alama ce ta goyon baya da kulawar da Hon. Rurum ke nunawa ga ‘yan jarida, musamman a cikin watan azumi.

KAROTA Ta Yi Kira Ga Direbobi Da Su Yi Tuki Cikin Hankali A Lokacin Azumin Ramadan

“Wannan tallafi na nuni da  yadda Hon. Rurum ke martaba aikin jarida da kuma goyon bayan walwalar ‘yan jarida a wannan lokaci mai albarka,” in ji sanarwar.

Advertisement

Kungiyar ta jaddada cewa irin wannan tallafi na ƙarfafa dangantaka da haɗin kai tsakanin masu ruwa da tsaki da kafofin watsa labarai, tare da yin kira ga sauran shugabanni da su yi koyi da hakan

NORP ta yi addu’a ga Hon. Rurum, tana fatan Allah Ya saka masa da alheri da ci gaba da ba shi nasara wajen wakiltar al, ‘umma.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending