Connect with us

News

NANS Zata Yi Zanga-zanga Kan Rufe Makarantun Boko A Wasu Jihohin Arewa Saboda Azumin Ramadan

Published

on

FB IMG 1740992015862

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Kungiyar Dalibai ta Kasa (NANS) ta bayyana shirin gudanar da zanga-zanga don kalubalantar matakin rufe makarantu a wasu jihohin arewa saboda Azumin Ramadan.

Advertisement

Jihohin da abin ya shafa sun hada da Kano, Bauchi, Kebbi da Katsina, inda gwamnatocin jihohin suka bayar da hutun don saukaka wa al’umma, musamman malamai, wahalhalun Azumin.

AZUMI: Darasi Na Hakika Ga Rayuwar Dan Adam

NANS ta ce matakin rufe makarantu zai hana dalibai cigaba da karatu, tare da jefa su cikin rashin sanin makomar karatunsu.

Advertisement

 

Itama Kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) ta yi Allah wadai da wannan mataki, tana mai cewa bai dace a daina karatu saboda Azumi ba, musamman a cikin wata mai muhimmanci kamar watan Ramadan.

Advertisement

Kungiyoyin biyu na kira ga gwamnatocin jihohin da su janye wannan doka domin bai wa dalibai damar cigaba da karatunsu ba tare da katsalandan ba.

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending