Connect with us

News

Gwamnan Kano ya kafa kwamitin binciken karbar belin wanda ake zargi da harkar kwayoyi da Kwamishina ya yi.

Published

on

1753396125570

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya kafa kwamitin bincike kan tsaya wa wani da ake tuhuma da safarar miyagun ƙwayoyi a gaban kotu da Kwamishinan Sufuri na jihar, Alhaji Ibrahim Namadi ya yi.

Wannan na cikin sanarwar da Babban Daraktan Yada Labaran gwamnan Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Asabar 26 ga Yuli, 2025.

Advertisement

Danwawu ya tsere bayan wanda ya tsaya masa a kotu ya janye

Sanarwar ta ce matakin na gwamna ya biyo bayan bayyanar sunan kwamishinan a cikin takardun belin wani da ake zargi da laifin safarar ƙwayoyi, wanda ya tayar da kura a cikin al’umma da kafafen sada zumunta.

Kwamitin da aka kafa zai kasance ƙarƙashin mai ba gwamna shawara kan harkokin shari’a, Barista Aminu Hussain, domin gudanar da bincike tare da bayar da shawarwari daidai da abin da suka gano.

Advertisement

Gwamna Abba ya ce gwamnatinsa ba za ta lamunci duk wani abu da zai zubar da kimar gwamnati ba, inda ya jaddada aniyar yaki da safarar miyagun ƙwayoyi da sauran laifuka a fadin jihar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending