News
Gwamnan Kano ya kafa kwamitin binciken karbar belin wanda ake zargi da harkar kwayoyi da Kwamishina ya yi.
Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya kafa kwamitin bincike kan tsaya wa wani da ake tuhuma da safarar miyagun ƙwayoyi a gaban kotu da Kwamishinan Sufuri na jihar, Alhaji Ibrahim Namadi ya yi.
Wannan na cikin sanarwar da Babban Daraktan Yada Labaran gwamnan Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Asabar 26 ga Yuli, 2025.
Sanarwar ta ce matakin na gwamna ya biyo bayan bayyanar sunan kwamishinan a cikin takardun belin wani da ake zargi da laifin safarar ƙwayoyi, wanda ya tayar da kura a cikin al’umma da kafafen sada zumunta.
Kwamitin da aka kafa zai kasance ƙarƙashin mai ba gwamna shawara kan harkokin shari’a, Barista Aminu Hussain, domin gudanar da bincike tare da bayar da shawarwari daidai da abin da suka gano.
Gwamna Abba ya ce gwamnatinsa ba za ta lamunci duk wani abu da zai zubar da kimar gwamnati ba, inda ya jaddada aniyar yaki da safarar miyagun ƙwayoyi da sauran laifuka a fadin jihar.
-
News23 hours ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
-
News2 days ago
Ana Zargin Matar Aure Da Shaƙe ’Yar Kishiyarta Mai Shekara 3 Har Lahira
-
News6 days ago
KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli
