Connect with us

News

Akalla Mutum 6  Sun Mutu Sanadiyyar Turmutsitsin Wurin Bauta A Indiya

Published

on

71753423 803
Mutanen sun je neman tabarruki ne a wani shahararren wurin bauta na mabiya addinin Hindu da ke cika a kowane mako.

Akalla mutum shida sun mutu a wani turmutsitsi da ya auku a wani shahararren wurin bauta na mabiya addinin Hindu a arewacin Indiya.

Hukumomin yankin sun sanar a ranar Lahadi cewa akwai mutane da dama da suka jikkata sakamakon fitar dango da masu neman tabarruki suka yi a wajen bautan a ranar Lahadi.

Advertisement

Gyaran Kundin Tsarin Mulki: Yadda Shafin Facebook na DSP Barau Ya Jawo Hankalin Jama’ar Arewa maso Yamma

Lamarin ya faru ne a birnin Haridwar, inda ake yawan zuwa bauta bayan wani layin wutar lantarki mai karfin gaske ya fado a kan wata hanya kusa da wurin bautan.

Lamarin ya jefa masu ibada da dama cikin firgici inda mutane suka rika neman tsira da rayukansu.

Advertisement

Wani babban jami’in gwamnati a jihar Uttarakhand, Vinay Shankar Pandey ya tabbatar da mutuwar mutane shida, ya kuma ce masu ibadar sun fara guje-guje don tsira bayan faruwar lamarin.

Jami’an yankin sun ce dubban masu ibada ne suka taru a wajen da ke kan tsauni, wanda ya shahara wajen karbar bakuncin masu ibada na Hindu, musamman a karshen mako da kuma ranakun bukukuwa.

Advertisement

 

 

Advertisement

DW

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending