News
Hadarin Mota Ya Yi Ajalin Mutum 9 Yan Garin Dambatta A Hanyar Dawowa Daga Daurin Aure
Mutane tara ne suka rasa rayukansu a wani mummunan hatsarin mota da ya auku a kan babban titin Katsina zuwa Kano.
Lamarin ya faru ne a ranar Asabar, 26 ga watan Yuli, 2025, kamar yadda wani mazaunin Dambatta a jihar Kano, Basiru Lawan, ya shaida manema Labarai
Akalla Mutum 6 Sun Mutu Sanadiyyar Turmutsitsin Wurin Bauta A Indiya
Ya ce mutanen da abin ya rutsa da su dukkansu ‘yan karamar hukumar Dambatta ne, kuma sun dawo ne daga wani bikin aure da aka gudanar a jihar Katsina.
Hatsura a kan manyan titunan Najeriya na ci gaba da zama babban barazana ga rayuwar matafiya, inda aka ruwaito mutuwar fiye da mutane 14 kwanan nan a wani hadari da ya jawo gobara.
Haka kuma, watanni biyu da suka gabata, ‘yan wasa fiye da 20 daga jihar Kano sun mutu a wani hatsarin mota yayin da suke tafiya gasar ƙasa.
