Connect with us

News

Talauci Ne Ya Haifar Da Matsalolin Tsaro A Arewacin Najeriya – Gwamnan Jigawa

Published

on

images

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya ce talauci ne babban dalilin da ya haifar da matsalolin a Arewa.

Ya bayyana haka ne a Kaduna lokacin bikin cika shekaru 25 da kafa Ƙungiyar Arewa Consultative Forum (ACF).

Advertisement

Kwastam Za Ta Fara Gwajin Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi Ga Sabbin Jami’ai Da Tsofaffi — CGC Adeniyi

Wannan ya fito ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Hamisu Mohammed Gumel, ya fitar.

Gwamna Namadi ya ce ko da yake matsalar tsaro babbar barazana ce, dole a magance tushen matsalar, musamman talauci, ta hanyar amfani da tsare-tsaren tattalin arziƙi na dogon lokaci.

Advertisement

Ya bayyana cewa Arewa tana da albarkatun ƙasa, ƙasar noma, da ɗimbin ma’aikata.

 

Advertisement

LABARAI MASU NASABA

Don haka, akwai damar kawar da talauci ta hanyar bunƙasa harkar noma.

Advertisement

A cewarsa, yawancin matsalolin tsaro suna da nasaba da talauci, kuma Arewa ba ta da hujjar ci gaba da kasancewa cikin talauci kasancewar tana da albarkatu da dama.

Saboda haka ne shugabannin Arewa ke himmatuwa wajen inganta noma.

Advertisement

Gwamnan ya yi imanin cewa gyare-gyaren da ACF, Gwamnonin Arewa, da Gwamnatin Tarayya ke goyon baya za su taimaka wajen sauya tsarin noma da farfaɗo da tattalin arziƙin yankin.

Ya ƙara da cewa bunƙasa noma zai samar da ayyukan yi da hanyoyin dogaro da kai ga miliyoyin mutane, kuma wajibi ne shugabanni su haɗa kai domin cimma wannan buri.

Advertisement

Gwamna Namadi ya taya ACF murna bisa cika shekaru 25 da kafuwa, sannan ya yaba da rawar da ta ke takawa wajen inganta zaman lafiya, haɗin kai, da ci gaba a Arewa da Nijeriya baki ɗaya.

 

Advertisement

 

LEADSHIP HAUSA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending